Wednesday, March 18
Shadow

Shugaban Sojojin Najeriya ya bayyana masu daukar nauyin matsalar tsaro da abinda suke son cimmawa a Najeriya

Shugaban hedikwatar tsaro ta kasa, Christopher Musa ya zargi cewa, yawaitar matsalar tsaron da ake fama da ita a Najeriya na da alaka da gabatowar zaben 2027.

Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV.

Yace idan ba haka ba, ta yaya, shekarar data gabata an samu rahoton raguwar matsalar tsaro sosai amma a wannan shekarar abubuwa su kara dagulewa?

Yace ‘yan siyasa ne ke daukar nauyin ‘yan Bindigar inda ya kara dacewa abinda suke son cimma shine bata sunan Gwamnati ace bata kokari.

Yace amma abin takaici shine ta yaya zaka rika kashe mutanen da kake son mulka?

Karanta Wannan  Wada Mutuniyar Maiwushirya tace taga an daina mata like da comment da share a videos din da take yi, dan haka tana neman a dawo a ci gaba da yi dan darajar Annabi(sallallahu Alaihi Wasallam)

Ya kuma zargi cewa, bayan masu daukar nauyin ‘yan Bindigar a cikin gida, akwai kuma masu daukar nauyin ‘yan Bindigar daga kasashen waje.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *