
Masu sharhi akan al’amuran tsaro na sukar shuwagabannin hukumomin tsaro na Najeriya saboda yawaitar kashe-kashen da ake yi musamman a jihohin Arewa.
Ana ganin matsalar tsaron ta sha kan su ko kuma basa daukar matakan da ya kamata dan magance matsalar.
Hakan na zuwanw yayin daka yi kashe-kashe a jihohin Filato, Borno, Katsina, da Benue.
Hakanan ga kuma wata sabuwar kungiyar masu ikirarin jihadi me suna Mamuda data bayyana a jihar Kwara dake arewa maso tsakiyar Najeriya.
Manyan shuwagabannin hukumomin tsaro a Najeriya sune Gen. Christopher Musa; Chief of Army Staff, Lt-Gen. Olufemi Oluyede; Chief of Air Staff, Air Marshal Hassan Abubakar, Chief of Naval Staff, Vice Admiral Emmanuel Ogalla.
Sannan akwai babban me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu da Ministan Tsaro, Muhammad Badaru da karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle.
An kashe mutane 250 a cikin sati biyu da suka gabata a jihohin Plateau, Benue, Borno, Kebbi, Katsina, Abia, da Kwara.
Jihar Plato ce ta fi fuskantar matsalar inda aka kashe mutane 113.
A jihar Benue kuma mutane 55 ne aka kashe.
Sai kuma a jihar Kwara aka kashe mutane 15.
Lamarin tsaron yasa mutane na kira ga hukumomi da su dauki mataka kawo karshen matsalar.