Friday, December 26
Shadow

Subhanallahi: Ji yanda ‘yansandan Najeriya suka kama wani limamin Masallaci na bata rayuwar karamar yarinya

Yan sanda a jihar Osun sun kama wani limamin masallaci me suna Babasanya-Araka da zargin yin lalata da karamar yarinya.

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Lamarin ya farune a garin Ede na jihar, kuma ya tayar da hankulan jama’ar garin.

Mutane sun taru suka fara dukan limamin saidai jami’an tsaro sun je sun kwaceshi.

Kakakin ‘yansandan jihar, Abiodun Ojelabi ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace da suka je Wajan har Amotekun sun kama limamin inda suka damka musu shi.

Yace zasu gudanar da bincike akanshi kamin su mika shi zuwa SCID.

Wani shaida yace yarinyar da ake zargin limamin da yin lalata da ita shekarunta 8 kuma ta bace ana nemanta sai gata an ganta tana kuka jini na zuba a gabanta.

Karanta Wannan  Ƴan Bìñďiga Sun Ķàšhe Dan Kasuwa, Alhaji Sabi'u Salihu Mai Hula Bagari Funtua, Akan Hanyarsa Ta Dawo Wa Funtua Daga Jihar Zamfara

Yace Tuni ka kaita Asibiti.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *