Thursday, February 26
Shadow

Tàshìn Bòm Ya Raunata Yara Sama da 5 a Garin Mafa Dake Jihar Borno, daya hannunsa ya cire

Yara 5 ne suka jikkata bayan tashin wani bam a karamar hukumar Mafa dake jihar Borno inda hannun daya daga cikin yaran ya tsinke.

Lamarin ya farune ranar alhamis da misalin karfe 2:25 na rana inda yaran suka je suna wasa da Bam din ba tare da sun sani ba.

Bam din dai an boyeshi ne a cikin bulo a kusa da inda ake gina Masallacin Juma’a na Mafa.

Yaran su 4 ne sai yarinya 1 Abdullahi Umar, Musa Mele, Fatima Abatcha, Abba Kawu Muhammed, da Khalid Alhaji Bukar.

Daya daga cikin yaran ya rasa hannun shi inda kuma aka garzsya da guda 4 zuwa Asibitin Maiduguri amma guda daya da hai ji ciwo sosai ba an kaishi Asibitin Mafa inda aka bashi magani aka sallameshi.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Ta dauki hankula saboda rawar Bhadala sanye da Hijabi

Tuni ‘yansanda da suka kware wajan kwance Bam suna kai dauki wajan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *