Thursday, December 25
Shadow

Tinubu Rahama ne ga Najeriya, Ya hana mutane da yawa mutuwa>>Inji Kungiyar kare muradin Yarbawa ta YCG

Kungiyar kare muradun yarbawa ta YCG ta bayyana shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaba na gari wanda rahama ne ga ‘yan Najeriya.

Kungiyar tace tsare-tsaren shugaba Tinubu sun taimaka wajan samar da tsaro, ga rayuwa da dukiyoyin jama’a.

Kungiyar tace a cikin shekaru 2 da shugaba Tinubu yayi yana mulki, Gwamnatinsa ta samar da tsaro da kara karfin tattalin arzikin Najeriya.

Wakilan Kungiyar Olugbemga Oyewusi, Mrs Buky Tunde Oshunrinde, ne suka bayyana hakan a sanarwar da suka fitar ga manema labarai.

Sun ce Yabo Shugaba Tinubu ya cancanta ba barazana da zagi ba.

Karanta Wannan  Na yi iya lissafin da zan yi na gano cewa, Tinubu ba zai ci zaben 2027 ba, na kudu zai zo>>Inji El-Rufai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *