Thursday, January 15
Shadow

Tinubu Rahama ne ga Najeriya, Ya hana mutane da yawa mutuwa>>Inji Kungiyar kare muradin Yarbawa ta YCG

Kungiyar kare muradun yarbawa ta YCG ta bayyana shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaba na gari wanda rahama ne ga ‘yan Najeriya.

Kungiyar tace tsare-tsaren shugaba Tinubu sun taimaka wajan samar da tsaro, ga rayuwa da dukiyoyin jama’a.

Kungiyar tace a cikin shekaru 2 da shugaba Tinubu yayi yana mulki, Gwamnatinsa ta samar da tsaro da kara karfin tattalin arzikin Najeriya.

Wakilan Kungiyar Olugbemga Oyewusi, Mrs Buky Tunde Oshunrinde, ne suka bayyana hakan a sanarwar da suka fitar ga manema labarai.

Sun ce Yabo Shugaba Tinubu ya cancanta ba barazana da zagi ba.

Karanta Wannan  Mutumin da ya auri mata 3 a rana daya, yayi bayanin yanda zai gamsar da kowacce daga cikinsu a gado

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *