Wednesday, March 18
Shadow

Tinubu ya amince da biliyan 16 don sake gina gadar Mokwa – Mohammed Idris

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da kashe naira biliyan 16.7 domin sake gina gadar Mokwa da ke jihar Neja a tsakiyar ƙasar, wadda ambaliya ta lalata.

Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris ne ya bayyana hakan a yau Asabar, yayin da shi kuma Ministan Ayyuka David Umahi ya ce shugaban ya amince da yin irin wannan aiki a jihohi da dama.

“Muna godiya ga shugaban ƙasa da minista [na ayyuka]. Tattaunawa kawai muka yi da shi kafin mu je wajen shugaban ƙasa, wanda shi kuma ya amince. Abu ne mai muhimmanci ga al’umma,” a cewar Idris.

Umahi ya ce sauran jihohin da za a yi aikin sun ƙunshi gadar Wukari a jihar Taraba, da gadar Lokoja a jihar Kogi, da gadar Afikpo a jihar Ebonyi, da gadar sama ta Keffi a jihar Nasarawa, da gadar Jebba a Kwara, da gadoji bakwai a jihar Edo, da kuma wata gada a jihar Kebbi.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon: Kalaman da Sheikh Lawal Triumph ya fadi akan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) Sam basu dace ba, kuma nasan zaku ce ni dan fim ne be kamata in saka baki ba, to Ku sani Annabu aka taba>>Inji Bosho

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *