Friday, December 26
Shadow

‘Yan majalisar Wakilai 2 sun bar jam’iyyar PDP da Labour Party zuwa APC

‘Yan majalisar wakilai biyu, Peter Akpanke, da Paul Nnamchi sun bar jam’iyyunsu inda suka koma jam’iyyar APC.

Akpanke ya fito daga jihar Cross River ne kuma an zabeshi a karkashin jam’iyyar PDP amma yanzu ya bar jam’iyyar zuwa APC.

Shi kuwa Nnamchi ya fito daga jihar Enugu ne kuma an zabeshi a karkashin jam’iyyar Labour party ne amma yanzu ya koma jam’iyyar APC.

Kakakin majalisar, Tajuddeen Abbas ya sanar da komawarsu APC a yayin zaman majalisar ranar Talata.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Wike ya bayyana cewa ranar 18 ga watan September Gwamnan Jihar Rivers, Simi Fubara da majalisar jihar zasu koma bakin aiki

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *