Thursday, May 8
Shadow

YANZU-YANZU: Gwamna Bago Ya Sanya Dokar Ta Baci A Garin Minna Biyo Bayan Rikìçe-Ŕikicen Ta Ta’ďdançi

Gwamnan jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, ya sanya dokar taƙaita zairga-zirgar baburan haya daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe a Minna babban birnin jihar sakamakon yawaitar rikicin ‘yan daba a birnin.

A cewar gwamnan, yanzu haka an takaita zirga-zirgar ‘yan acaɓa da babura masu ƙafa uku a wannan tsakanin.

Bago ya bayyana hakan ne yayin wani muhimmin taron tsaro da masu ruwa da tsaki suka yi da sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro a gidan gwamnati yau Talata.

”Babu wanda zai sake ɗaukar kowane irin nau’i makami a garin Minna. Ina bai wa jami’an tsaro umarni, duk mutumin da kuka gani da makami ku ɗauke shi a matsayin ɗanfashi da makami.” in ji shi.

Karanta Wannan  Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya kaiwa tsohon kwamishinansa, Bashir Sa'idu dake daure a gidan yari kan zargin satar sama da Naira Biliyan 3 ziyara

Ya bayyana cewa sabon matakin na da nufin daƙile matsalolin tsaro da ke ƙara taɓarɓarewa a babban birnin jihar.

Ya kuma umurci hakimai da dagatai da masu unguwanni da su fara aikin tantance duk wasu baƙi da ke shiga yankunansu.

Ya kuma yi gargaɗin cewa za a ruguza duk wani gida da aka samu yana ɗauke da waɗanda ake zargi da aikata laifuka ko kuma masu safarar miyagun ƙwayoyi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *