Monday, June 2
Shadow

Yarabawa miliyan 60 sun shirya ficewa daga Najeriya – Akintoye

Shugaban Ƙungiyar Ƙudirin samar da ‘Yancin Kai ta Yarbawa, Farfesa Banji Akintoye, ya jaddada cewa ƙungiyar ba za ta janye daga neman kafa ƙasar Yarabawa ba.

A cewar Akintoye, kimanin Yarabawa miliyan 60 ciki har da mazauna gida da ‘yan ƙasashen waje, suna goyon bayan ƙudirinsa na kafa ƙasar Yarbawa a matsayin ƙasa mai cin gashin kanta.

Da ya ke tattaunawa da jaridar The PUNCH a jiya Litinin, Akintoye ya ce, “Ba za mu koma baya ba. Dole ne mu fice daga Najeriya, ko kuma ƙasarmu za ta shiga matsala.

“Ba kwa jin muryar mu a tituna? Ƙasar Yarabawa yanzu, babu gudu ba ja da baya.

Karanta Wannan  DOLE MU YI JINJINA A GARE SU: Sun Biya Dukkan Bashin Da Ake Bin Marigayi Sheik Idris Da Kudin Aljihunsu

“Muna nufin Yarabawa da ke Nijeriya, kusan mutane miliyan 55 zuwa 60. Muna so mu kafa ƙasa ta kanmu. Ba za a samu Najeriya ba idan muka kafa ƙasarmu. Amma idan sauran suna son ci gaba da kasancewa a matsayin Najeriya, babu matsala,” in ji shi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *