Thursday, January 15
Shadow

Yayin da Dalibai Kiristoci ke zargin an hanasu gona coci a jami’o’in Kashere, Gombe dana BUK, Kano, Shima wani dalibi musulmi yayi zargin cewa an hana Musulmai gina masallaci a jami’ar Jos, UniJos

A dazu ne hutudole ya kawo muku rahoton yanda wasu Kiristoci dalibai daga jami’o’in BUK, Kano da Kashere, Gombe inda suke zargin an hanasu gina coci a wadannan makarantu yayin da aka bar musulmai suka gina masallatai.

A martani ga wannan zargi shima wani dalibi musulmi yai zargin cewa an hana dalibai musulmai gina masallaci a jami’ar UNIJos, dake jihar Filato.

Yace duk da akwai masalacin da aka fara ginawa amma an hana a karasashi.

Sannan yayi zargin cewa an ma hana musulmai yin salla a masallacin da ba’a karasa ba.

Karanta Wannan  Mun samu nasara sosai akan tshageran Dhaji amma kalaman Shugaban Amurka, Trump ya sa suka samu karfin Gwiwar dadowa har suka dauke daliban jihar Kebbi>>Inji Gwamnatin tarayya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *