Friday, January 16
Shadow

Yayin da Wutar Lantarki ta gagari Gwamnatin tarayya gyarawa, Shugaba Tinubu yayi sabuwar doka da ta baiwa Jihohi ragamar samar da wutar Lantarki a Najeriya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa sabon daftarin doka hannu wanda ya baiwa jihohin Najeriya damar samarwa da rarraba wutar Lantarki a jihohinsu.

Tun a shekarar 2024 daftarin dokar ya wuce amincewar ‘yan majalisa inda ake jiran shugaba Tinubu ya saka hannu amma bai saka ba sai a yau.

Masana sun ce hakan ya canja kula da wutar lantarki a Najeriya wanda a baya yake hannun Gwamnatin tarayya, a yanzu jihohi ne zasu rika samar da wutar.

Hakanan ana tsammanin wannan sabuwar dokar zata jawo masu zuba jari a harkar sannan zata karfafa gasa tsakanin jihohin wanda hakan zai inganta samar da wutar Lantarkin.

Karanta Wannan  Ya Zama Wajibi Ga Ƴan Nijeriya Mu Tashi Tsaye Wajen Ganin An Kawar Da Gwamnatin APC 2027 A Kowane Matakai, Saboda Mawuyacin Halin Da Ta Jefa Mu, Ta Hanyar Haɗaka Da Muke Shirin Kafawa Nan Gaba Kaɗan, Cewar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *