Friday, December 26
Shadow

Yayin da Wutar Lantarki ta gagari Gwamnatin tarayya gyarawa, Shugaba Tinubu yayi sabuwar doka da ta baiwa Jihohi ragamar samar da wutar Lantarki a Najeriya

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sakawa sabon daftarin doka hannu wanda ya baiwa jihohin Najeriya damar samarwa da rarraba wutar Lantarki a jihohinsu.

Tun a shekarar 2024 daftarin dokar ya wuce amincewar ‘yan majalisa inda ake jiran shugaba Tinubu ya saka hannu amma bai saka ba sai a yau.

Masana sun ce hakan ya canja kula da wutar lantarki a Najeriya wanda a baya yake hannun Gwamnatin tarayya, a yanzu jihohi ne zasu rika samar da wutar.

Hakanan ana tsammanin wannan sabuwar dokar zata jawo masu zuba jari a harkar sannan zata karfafa gasa tsakanin jihohin wanda hakan zai inganta samar da wutar Lantarkin.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo:Jama'ar Katsina ku yi Hakuri, kamin in hau mulki na yi Alkawarin duk wata zan rika bada bayanin yawan kudaden da muka samu da yawan wanda muka kashe, amma yanzu da na zama Gwamnan naga abin ba zai yiyu ba>>Inji Gwamnan Jihar Katsina Dikko Radda

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *