Thursday, February 5
Shadow

Za’a rage farashin kiran waya dana data daga kaso 50 zuwa kaso 35

Rahotannin da kafar hutudole ta samu na cewa, za’a rage farashin kudin kiran waya dana data daga kaso 50 da aka kara zuwa kaso 35.

Hakan ya bayyanane a cikin jawabin da shugaban kungiyar NLC ya fitar inda suke barazanar shiga yajin aiki idan ba’a yi wannan ragi ba.

Hutudole ya faimci cewa, an yi zama tsakanin Gwamnatin tarayya da masu ruwa da tsaki a bangaren tsaro inda aka cimma matsaya gane da karin kudin kiran waya dana data, maimakon kaso 50 cikin 100 da aka yi, yanzu zai koma kaso 35 cikin 100.

Kungiyar NLC tace idan ba’a tabbatar da wannan kari ba, zata tafi yajin aiki.

Karanta Wannan  Soyayyar Da Nake Yi Wa Tinubu Da Shettima Ta Sa An Je Har Wurin Sana'ata An Sace Min Turaren Da Nake Siyarwa, Don Haka Daga Yau Na Bar Tafiyar Tinubu/Shettima, Inji Bashir Musa Maiturare Daga Garin Nguru, Jihar Yobe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *