Tuesday, May 13
Shadow

Ƙasa ta rufe mutum 30 a mahaƙar ma’adanai ta jihar Neja

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Neja a Najeriya (NSEMA) ta ce kimanin mutum 30 ne ake fargabar sun mutu sakamakon zaftarewar kasa da ta auku a wani wurin hakar ma’adinai.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Galkogo na ƙaramar hukumar Shiroro.

Hukumar ta ce an kuma samu nasarar ceto mutum shida da rai, sai dai sun samu munanan raunuka.

Mahakar dai ta rufta ne a jiya Litinin lokacin da suke tsaka da aiki haƙar ma’adanai.

Latsa hoton ƙasa ku saurari rahoton Zubairu Ahmad:

Karanta Wannan  Gwamnin ban tausai:Ji yanda mutane suka nutse a ruwa yayin da suka shiga kwale-kwale dan tserewa harin 'yan Bin-di-ga a jihar Naina

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *