Thursday, May 22
Shadow

Tsagin NNPP ya caccaki Kwankwaso bisa sukar waɗanda su ka bar jam’iyyar zuwa APC a Kano

Tsagin NNPP ya caccaki Kwankwaso bisa sukar waɗanda su ka bar jam’iyyar zuwa APC a Kano.

Wani tsagi na jam’iyyar NNPP, ya caccaki Sanata Rabi’u Kwankwaso kan yadda ya bayyana ‘ya’yan kungiyar Kwankwasiyya da suka koma APC a matsayin maciya amana, inda ta ce Kwankwaso ne maciya amana.

A tuna cewa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya na kasa, ya caccaki wasu jiga-jigan jam’iyyar NNPP a jihar Kano, wadanda kwanan nan suka sauya sheka zuwa APC, inda ya bayyana abin da suka yi a matsayin cin amana.

Kwankwaso ya bayyana haka ne a gidansa da ke Miller Road da ke Kano a yammacin ranar Juma’a, a lokacin da wasu ’yan kungiyar kwankwasiyya daga karamar hukumar Takai suka ziyarce shi.

Karanta Wannan  Darajar wasu kuɗaɗen kirifto ta tashi bayan sanarwar Donald Trump

A wata sanarwa da ya fitar a yau Litinin a Legas, Shugaban NNPP na kasa, Dr Agbo Major ya ce Kwankwaso ba shi da ikon yin magana a madadin jam’iyyar.

“An kori Sanata Rabiu Kwankwaso daga jam’iyyar NNPP tare da mabiyansa karkashin jagorancin Dr Ahmed Ajuji.”

A cewar Major, Kwankwasiyya ba jam’iyyar siyasa ba ce, kungiya ce da ta shiga jam’iyyar NNPP bayan zaben shugaban kasa na 2023 inda shugabansu ya zama mai rike da tutar jam’iyyar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *