
Sanata Godswill Akpabio wanda shine kakakin majalisar dattijai ya bayyana cewa, abinda Sanata Natasha Akpoti ta yi zai sa a fara jin tsoron baiwa mata mukaman siyasa.
Ya bayyana hakanne inda yace yanzu da Kamala Harris ta yi irin wannan abin da Sanata Natasha Akpoti ta yi da zata kai matsayin mataimakiyar shugaban kasa?
Yace amma yana kira ga mutane da kada laifin wani ya shafi wani, yace yana da ‘ya’ya mata 4 yana son a goyi bayansu da basu dama su kai matsayi babba dama sauran mata na Najeriya.