Friday, December 5
Shadow

‘Yan Bìndìga ne ke mulkar Najeriya>>Inji Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai

Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, ‘yan Bindiga ne ke mulkar Najeriya.

El-Rufai yace dan haka Najeriya na cikin tsaka mai wuya.

El-Rufai yace ‘yan Najeriya na ci gaba da maimaita kuskuren da suka yi a baya na zabar shuwagabannin da bana gari ba.

Ya bayyana hakane a babban birnin tarayya, Abuja ranar Asabar a wajan wani taro.

Yace Najeriya na cikin matsalar da bata taba shiga ba tun shekarar 1914 a yayin sa aka hade Arewa da kudu.

Yace mafi yawancin shuwagabannin basu san yanda zasu gudanar da mulki ba kawai su dai su samu mulkin shine a gabansu.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya baiwa kowacce daga cikin 'yan matan kungiyar kwallon kafa ta Najeriya, Super Falcons Naira Miliyan dari da hamsin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *