Friday, December 26
Shadow

IMF tace tattalin arzikin Najeriya zai samu habaka

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta hasashensa kan bunƙasar tattalin arzikin Najeriya na shekarar 2025 da 2026.

IMF ya bayyana sabon hasashen a watan Yulin da muke ciki wanda a ciki ya yi ƙiyasin samun ƙarin bunƙasar tattalin arzikin Najeriya.

Asusun ya yi hasashen samun jarin bunƙasar tattalin arzikin Najeriya da kashi 3.4 a 2025, ƙari a kan hasashen kashi 3.0 da ya yi a watan Afrilu.

Haka kuma IMF ya yi hasashen cewa tattalin arzikin Najeriya zai samun ƙarin baunƙasa da kashi 3.2 a 2026, saɓanin hasashen kashi 2.7 da ya yi a watan na Afrilu.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon wasu na rokon Kabarin Shehu ya kawowa Najeriya saukin tsadar man fetur ya dauki hankula

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *