Thursday, February 26
Shadow

Gwamnatin tarayya tace zata rama tsaurara Yin Bizar da kasar Amurka ta kakabawa ‘yan Najeriya

Gwamnatin kasar Amurka tace duk dan Najeriyar dake neman Visa ta shiga kasarta dolene ya nuna yanda yake amfani da kafafen sadarwa na tsawon shekaru 5 baya.

Dokar tace kin yin hakan zai iya sa a hana mutum Visar shiga kasar Amurkar.

Saidai cikin gaggawa, Gwamnatin taraya ta sha Alwashin daukar irin wannan mataki akan ‘yan kasar Amurka masu shigowa Najeriya.

Kasar Amurka ta bayyana wannan sabuwar dokane ta kafar X wanda tace hakan na daga cikin shirin shugaban kasarta, Donald Trump na ganin ya samarwa kasar tasa tsaro.

Me magana da yawun ma’aikatar tsaro ta Najeriya, Kimiebi Ebienfa ya bayyana cewa, Gwamnatin kasar Amurka tuni ta sanar dasu wannan shiri.

Karanta Wannan  Kwankwaso yayi karin haske kan Rahoton cewa ya amincewa Abba ya koma jam'iyyar APC

Yace itama Najeriya zata dauki irin wannan mataki akan ‘yan kasar Amurka masu neman Visa a Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *