Friday, December 26
Shadow

Allah Sarki: Ji Yanda matar aure ta yanke jiki ta fadi sumammiya bayan da mijin ta ya saketa a Kotu, Ta kai karane inda tace Alkali ya hana mijin sakinta saboda bata so su ramu amma mijin yace shi baya sonta

Wata matar aure Mulikat Yusuf ta yanke jiki ta fadi sumammiya bayan da mijinata ya saketa a kotu duk da kai kara da ta yi akan kada ya saketa.

Matar ta kai mijinta, Ishaq Abdulganiyu kara inda tacewa kotu ta haifa masa yara 6 kuma ita yanzu idan ya saketa bata san inda zata ba.

Saidai mijin yace babu ruwansa da ita.

A hanyarta ta fita daga kotun ta yanke jiki ta fadi.

Saida aka yayyafa mata ruwa ta farfado.

Lamarin ya farune a kotun dake Igboro, Ilorin jihar Kwara.

Alkalin kotun, Toyin Oluko ya baiwa matar shawara ta je ta lallaba mijinta.

An daga ci gaba da sauraren shari’ar har zuwa 5 ga watan Disamba, inda alkalin yace ya basu damar su shirya kamin lokacin ko kuma a ci gaba da shari’a.

Karanta Wannan  Yanda Mutanen Karkara suka fi na Birni zuwa aikin Hajjijn bana ya kawo cece-kuce

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *