Friday, December 5
Shadow

Ku tashu tsaye ku kare kanku, Babu maganar biyan kufin fansa ko Sulhu>>Gwamnan Jihar Naija, Umar Bago ya gayawa mutanen jihar

Gwamnan jihar Naija, Umar Bago ya baiwa mutanen jiharsa shawarar su tashi tsaye su kare kansu.

Yace matsalar garkuwa da mutane dan neman kudin fansa a jihar ya kai matakin yaki inda yace dole sai an tashi tsaye.

Gwamnan yace, ba zai biya kudin fansa ba kuma babu maganar sulhu da ‘yan Bindigar yace idan aka rika basu kudi, zasu mayar da abin kasuwanci.

Gwamna Bago yace kundin tsarin mulkin Najeriya ya baiwa kowane dan kasa damar kare kansa da Dukiyarsa.

Karanta Wannan  Talauci alamace ta yawan zunubi da rashin tsoron Allah>>Inji Pasto Komayya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *