Thursday, December 25
Shadow

Gidan Talabijin din Channels TV na shan suka saboda yanda suka kawo Rahoton abinda ya faru a masallaci jiya a jihar Borno

Kafar Channels TV suna shan suka saboda yanda suka rubuta Rahoton abinda ya faru a masallaci a jihar Borno jiya.

Abin fashewa ya fashe a masalacin jihar Borno inda wasu suka rasa rayukansu, wasu kuma suka jikkata.

Saidai Channels TV a rahoton data kawo tace abin fashewar ya fashene a Maiduguri yayin da ake bikin Kirsimeti.

Da yawa dai sun zargi Channels TV da Munafurci saboda bas saka cewa a masallaci abinnya faru ba hakanan wasu na cewa babu abinda ya hada tashin abin fashewar da Kirsimeti tunda ba a coci ya faru ba.

Karanta Wannan  Ji Sautin Murya dake alamta cewa Hukumar 'yansanda ta jihar Kano ce ta kama yarannan da aka kai Kotu a Abuja sannan kuma Gwamnatin jihar Kano ma tasan da maganar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *