
Kungiyar ‘yan kwallon Najeriya ta Super Eagles da masu horas dasu sun ce ba zasu je wasan da zasu buga da Algeria ba idan ba’a biyasu hakkokinsu ba.
Kungiyar ta bayyana cewa akwai alkawuran kudaden da aka musu idan suka yi nasara a wasanni da kasashen Tanzania, Tunisia, Uganda, da Mozambique amma ba a cika musu wadannan alkawuran ba.
Kungiyar tace ba zata ke garin Marrakech ba ranar Alhamis dan yin Atisayen wasan da zasu buga da kungiyar kasar Algeria ba idan ba’a biyasu ba.
Najeriya dai zata yi wasan Quarter finals da kasar Algeria.