Friday, December 5
Shadow

ADC ba barazana bane: Cikin Sauki Tinubu zai samu kuri’u Miliyan 15 a zaben 2027 ya lashe zabe>>Inji wani na hannun damar shugaban kasar

Tsohon dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar APC, Nicolas Felix ya bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai samu kuri’u Miliyan 15 a zaben 2027.

Yace wannan babu tantama akai.

Ya bayyana hakane a yayin da ya rabawa wasu mabukata man fetur kyauta a Suleja dake jihar Naija ranar Alhamis.

Ya ce Hadakar ‘yan Adawa a ADC ba zata zamarwa Shugaba Bola Ahmad Tinubu barazana ba.

Ya kara da cewa, kamar yanda ‘yan Adawar suka taho suka hadu, haka kuma zasu watse.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon yanda babbar mota ta bi ta kan 'Yansandan Najeriya 2 ta kàshe su

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *