Thursday, April 10
Shadow

Al’ummar Kano Sun Zargi ‘Yansanda Da Yunƙurin Sanya Dokar Ta-baci Kan Gayyatar Sarki Sunusi

Al’umma Jihar Kano sun yi ikirarin cewa gayyatar da babban Sifetan ‘yansanda ya yi wa Sarki Sanusi wani bangare na shirin kafa dokar ta-baci a Jihar.

Hakan na zuwa ne biyo bayan rahotannin da ke cewa rundunar ‘yan sandan Najeriya ta gayyaci Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, a hukumance, zuwa ofishin ta dake Abuja domin bincike kan wani yamutsu da aka samu a lokacin bukukuwan Sallah.

Wasu ‘yan jihar da suka yi magana kan kama Usman Sagiru dan shekara 20 a ranar Lahadi, 30 ga Maris, 2025 da ke Sharifai Quarters dangane da zargin kisan wani dan banga a tawagar Sarki Sanusi Lamido Sanusi na biyu bayan Sallar Idi, sun bayyana cewa ba za su iya alakanta lamarin da gayyatar Sarki ba.

Karanta Wannan  Gwamnatin Sokoto ta ƙaddamar da tallafin azumi ga masu buƙata ta musamman

Takardar gayyata mai kwanan wata 4 ga Afrilu, 2025, kuma mai dauke da sa hannun CP Olajide Rufus Ibitoye, kwamishinan ‘yan sanda (Ayyuka), an bayar da shi ne a karkashin umarnin babban sufeton ‘yan sanda na ƙasa

Wasikar ta bukaci Sarki Muhammadu Sanusi II da ya kai kansa ga hedikwatar hukumar leken asiri da ke Abuja a ranar Talata 8 ga Afrilu, 2025 da karfe 10 na safe.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *