Friday, November 14
Shadow

Yansanda Sun Cafke Jami’insu Da Ya yi Barazanar Ramuwar Gayya Kan Kìsàn Mafarauta a Edo

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta cafke Hadaina Dan-taki, wanda ya yi barazanar kai hari ga ‘yan kudu a Arewa, domin daukar fansa kan mafarauta 16 da aka kashe a Uromi, jihar Edo.

Hakan ya biyo bayan cece-kucen da jama’a suka yi akan jami’an bayan wallafa sakon barazanar a shafinsa na Facebook.

Idan zamu iya tunawa dai dan sandan ya yi barazanar kai harin ramuwar gayya ga ‘yan kudancin Najeriya da ke zaune a arewacin Najeriya.

Kalaman Dan-Taki na zuwa ne a matsayin martani ga kashe ‘yan Arewa 16 da aka yi a garin Uromi dake Jihar Edo.

A wani zazzafan tsokaci da ya yi a Facebook ranar Talata, Dan-Taki ya rantse da Allah sai ya rama kisan da aka yiwa al’ummar Arewa, yana mai shan alwashin cewa ‘yan Arewa za su dauki kwakkwaran mataki kan ‘yan Kudu a nan gaba kaɗan.

Karanta Wannan  Kwana hudu da suka gabata na musulunta, amma ana gayamin za'a koreni daga wajan aiki na idan ban bar Musulunci ba, Saidai na zabi Allah da Addinin Musulunci maimakon aikin nawa>>Inji Ba'amurke, Martin

Don ƙarin bayani, za ku iya kallon cikakkun shirye-shiryenmu a kan decodan DStv lamba ta 393, startimes lamba ta 183 , Canal plus Niger @ 288 , da kuma decodan Gotv lamba ta 18.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *