Wednesday, May 21
Shadow

Ana Zargin Abokan Dan Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Jama’are, Isa Wabi Da Kašhè Shi A Yayin Da Suka Hauro Masa Gida Cikin Darè A Jihar Bauchi

Rundunar ‘yansandan Najeriya reshen jihar Bauchi ta ce ta kama mutum ɗaya bisa zargin kashe tsohon shugaban ƙaramar hukumar Jama’are Isa Wabi.

A cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Juma’a, waɗanda ake zargin abokan ɗansa ne kuma sun aikata kisan ne da tsakar daren yau a gidansa da ke Fadaman Mada.

Nan take aka kai shi asbitin Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa bayan rahoto ya ishe ‘yansandan cewa wasu matasa sun caccaka masa wuƙa a wuya.

“Binciken farko-farko ya nuna wasu mutum biyu ne suka aikata kisan waɗanda abokan ɗan Wabi ne ɗan shekara 24 mai suna Abdulgafar Isa Mohammed,” a cewar sanarwar.

Karanta Wannan  Hotuna: 'Yan Damfara sun cuci wannan matar Inda suka sayi shinkafa buhu 4 da kudin boge

Ta ce dakaru sun tarar da ɗaya daga cikin mutanen a sume kuma aka kai shi asibiti, inda daga baya aka tabbatar da mutuwarsa.

‘Yansanda sun ce sun kama Abdulgafar domin ci gaba da bincike.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *