Friday, December 5
Shadow

Ana Zargin Abokan Dan Tsohon Shugaban Karamar Hukumar Jama’are, Isa Wabi Da Kašhè Shi A Yayin Da Suka Hauro Masa Gida Cikin Darè A Jihar Bauchi

Rundunar ‘yansandan Najeriya reshen jihar Bauchi ta ce ta kama mutum ɗaya bisa zargin kashe tsohon shugaban ƙaramar hukumar Jama’are Isa Wabi.

A cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Juma’a, waɗanda ake zargin abokan ɗansa ne kuma sun aikata kisan ne da tsakar daren yau a gidansa da ke Fadaman Mada.

Nan take aka kai shi asbitin Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa bayan rahoto ya ishe ‘yansandan cewa wasu matasa sun caccaka masa wuƙa a wuya.

“Binciken farko-farko ya nuna wasu mutum biyu ne suka aikata kisan waɗanda abokan ɗan Wabi ne ɗan shekara 24 mai suna Abdulgafar Isa Mohammed,” a cewar sanarwar.

Karanta Wannan  Manyan Malaman Najeriya, Sheikh Daurawa, Bin Uthman, da Gidado Triumph sun roki Allah yasa kada gobarar kasar Israyla ta mutu

Ta ce dakaru sun tarar da ɗaya daga cikin mutanen a sume kuma aka kai shi asibiti, inda daga baya aka tabbatar da mutuwarsa.

‘Yansanda sun ce sun kama Abdulgafar domin ci gaba da bincike.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *