Sunday, December 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ji Dalilin da yasa Kasar Saudiyya ta hana Sheikh Dr. Ahmad Gumi yin aikin Hajjin bana, kamar yanda yayi karin bayani

Ji Dalilin da yasa Kasar Saudiyya ta hana Sheikh Dr. Ahmad Gumi yin aikin Hajjin bana, kamar yanda yayi karin bayani

Duk Labarai
Hukumomi a ƙasar Saudiyya sun hana babban malamin addinnin Musulunci a Najeriya, Sheikh Ahmad Gumi shiga ƙasar domin gudanar da aikin hajjin bana. Sheikh Gumi wanda ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa gwamnatin Saudiyya bayan ta ba shi bizar shiga ƙasar domin aikin Hajji amma kuma sai ba a ba shi damar shiga Madina domin fara aikin ibada ba. "Bisa waɗansu dalilai saboda ra'ayi na kan siyasar duniya, hukumomi a Saudiyya ba sa son kasancewata a Hajji duk da sun ba ni biza," in ji Sheikh Gumi kamar yadda ya wallafa a shafinsa na Facebook. Ya ƙara da cewa "Ina godiya ga hukumomi a Najeriya waɗanda suka sha alwashin tuntuɓar hukumomin Saudiyya a kan wannan lamarin." Bayanan da BBC ta tattaro sun nuna cewa Sheikh Ahmad Abubakar Gumi na cikin tawagar malaman da hukumar aikin hajjin...
Ji yanda wata mata ta kàshè kishiyarta a Garin Daura na jihar Katsina

Ji yanda wata mata ta kàshè kishiyarta a Garin Daura na jihar Katsina

Duk Labarai
Ƴan sanda a jihar Katsina sun kama wata matar aure da ake zargi da kashe kishiyarta. Lamarin ya faru ne a bayan wata makarantar firamare ta Dadi da ke unguwar Sabon Gari, a ƙaramar hukumar Daura bayan da wata matsala ta cikin gida tsakanin matan auren biyu ta rikiɗe zuwa rikici mai muni da ya kai ga mutuwa. Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya fitar a ranar Lahadi, inda ya bayyanawa manema labarai abin da ya faru. Sanarwar ta ce: “A ranar 24 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 11 na dare ne ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari suka samu rahoto daga wani Nasir Yusuf, mijin matar, cewa ya dawo gida daga kasuwa ya tarar da matarsa ta farko mai suna Zainab Lawal tana kwance cikin jini, an caka mata wuƙa sau da dama.” “Da sa...
Kalli Bidiyon yanda matar shugaban kasar Faransa ta fallamai mari a bainar jama’a

Kalli Bidiyon yanda matar shugaban kasar Faransa ta fallamai mari a bainar jama’a

Duk Labarai
Ana zargin Matar shugaban kasar Faransa Brigitte Macron ta falla masa mari a yayin da suke shirin sauka daga jirgin saman da ya kaisu kasar Vietnam. Suna cikin jirgin yayin da ana ganin shugaba Macron na magana da ita a yayin da ita kuma ba'a ganinta daga cikin jirgin sai aka ga hannunta ya falla masa mari. Da farko ya gigice amma daga baya ya nutsu sannan ya fito daga cikin jirgin yayin da ta bishi a baya. https://twitter.com/GlobeEyeNews/status/1926926455482515628?t=pTRahTVPqPda_RoSKBC0lQ&s=19 Yayi kokarin kama hannunta amma taki amincewa. Daga baya an ganshi cikin fushi. Lamarin ya dauki hankula a kafafen sada zumunta. Da farko ofishin Macron ya musanta Bidiyon da hotunan inda yace na bogi ne amma daga baya aka tabbatar na gaskiyane. Saidai masu magana da ...
Da Duminsa: Shugaban Amurka, Donald Trump na daf da cimma yarjejeniyar Tsagaita wuta tsakanin Israyla da Falasdiynawa

Da Duminsa: Shugaban Amurka, Donald Trump na daf da cimma yarjejeniyar Tsagaita wuta tsakanin Israyla da Falasdiynawa

Duk Labarai
Rahotanni dake fitowa daga gabas ta tsakiya n cewa, Shugaban kasar Amurka, Donald Trump na daf da sanar da cimma yarjejeniya tsakanin Israyla da Falasdiynawa. Saidai zuwa yanzu fadar White House bata ce komai kan lamarin ba. Dama dai a baya rahotanni sun bayyana cewa Bayan da matsi yayi yawa, Benjamin Netanyahu na shirin amince da Tsagaita wuta. Tuni dai kasashen Turai da suka hada da Faransa suka fara raba gari da Benjamin Netanyahu.
Gwamnatin Tinubu ta samu karin Naira Tiriliyan 7 bayan cire tallafin man fetur amma har yanzu Talakan Najeriya bai shaida ba

Gwamnatin Tinubu ta samu karin Naira Tiriliyan 7 bayan cire tallafin man fetur amma har yanzu Talakan Najeriya bai shaida ba

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa Jimullar Naira Tiriliyan 7 ne gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta samu bayan cire tallafin Man fetur. Saidai duk da haka, talakan Najeriya bai shaida ba inda ake ci gaba da fama da tsadar rayuwa da Talauci da matsalar tsaro. Wadannan karin kudade da aka samu an karawa gwamnatoci a kowane mataki watau Tarayya, jiha da kananan hukumomi yawan kudaden da suke samu. Sannan an sayo motoci masu amfani da Gas me Arha sannan an rabawa talakawa kudaden Tallafi sannan an kashe makudan kudade wajan gyaran matatun man fetur din da muke dasu amma duk da haka babu Alamar shaida hakan ga Talaka. Yawanci kasuwanci da kamfanoni musamman kanana da matsakaita sun rage ma'aikata wasu ma sun kulle inda Bankin Duniya, da IMF ke kara tabbatar da cewa akwai mutane ...
Munafurci Dodo: Rikici ya barke tsakanin Wike da Gwamna Makinde na jihar Oyo wanda sune suka hadewa Atiku kai suka ce ba zasu goyi bayanshi ba a zaben 2023

Munafurci Dodo: Rikici ya barke tsakanin Wike da Gwamna Makinde na jihar Oyo wanda sune suka hadewa Atiku kai suka ce ba zasu goyi bayanshi ba a zaben 2023

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa rashin jituwa da rikici ya barke tsakanin Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde da Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike. Rahoton yace An kafa kwamiti dan yin sulhu tsakanin su amma Wike ya fice daga sulhun da ake yi inda ya ke zargin Gwamna Seyi Makinde da Gwamnan Jihar Enugu da hannu a rikicin da ya mamaye jam'iyyar. Hakan na zuwane a yayin da jam'iyyar ke shirin yin babban taronta na masu ruwa da tsaki ranar 27 ga watan Mayu da muke ciki. Tuni Kwamitin Amintattu na jam'iyyar suka kira taron gaggawa a yau, Litinin dan shawo kan matsalar. A zaben shekarar 2023 dai Gwamna Seyi Makinde da Nyesom Wike na daga cikin gwamnoni 5 da suka hadewa Atiku ka sukace ba zasu goyi bayansa ba.
Ji yanda ‘yan Lùwàdì kewa kananan yara maza wayau suna aika musu hotunan Tsìràicìnsu, ana kasuwanci da hotunan ana sayarwa Turawa a Najeriya

Ji yanda ‘yan Lùwàdì kewa kananan yara maza wayau suna aika musu hotunan Tsìràicìnsu, ana kasuwanci da hotunan ana sayarwa Turawa a Najeriya

Duk Labarai
Wani abin ban mamaki da ya faru shine yanda aka gano wasu bata gari dakewa kananan yara maza wayau suna aika musu hotunansu tsirara. Yaran dai nantsakanin shekaru 14 zuwa 21 ne. Wasu daga cikinsu da saninsu ake aikata hakan saboda ana basu kudi, wasu kuma ba da saninsu ba saboda an musu wayau ne. Jaridar Punchng ta yi bincike akan lamarin kuma ta gano cewa ana amfani da kafafen sada zumunta ne irin su X ne wajan aikata wannan masha'a. Saidai ana ta kulle irin wadannan shafuka amma masu aikata wannan masha'a sai su kara bude wasu. Wasu yaran da a yanzu sun girma amma ana da Bidiyonsu suna cikin fargaba saboda a yanzu ana ta yada Bidiyon a kakafen sada zumunta wanda hakan yana zamar musu Abin Kunya. An yi kira ga gwamnati, da ta dauki matakai kan lamarin dan tsafta kafafen...
Bidiyo: Ni ba ‘yar Iska bace: Mansurah Isah ta bayyana hali na gari da yasa Sani Danja ya aureta

Bidiyo: Ni ba ‘yar Iska bace: Mansurah Isah ta bayyana hali na gari da yasa Sani Danja ya aureta

Duk Labarai
Tsohuwar tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah ta bayyana dalilin da yasa Tsohon Mijinta, Sani Danja ya aureta. Mansurah ta bayyana hakanne a wata hira da BBChausa ta yi da ita inda take cewa ita ba 'yar Iska bace. Tace da ita 'yar iska ce da Sani Danja bai Aureta ba. Kalli Bidiyon hirar: https://www.tiktok.com/@musaddeeqq_haysam/video/7508388274101046534?_t=ZM-8wfWYscDyDt&_r=1 Mansurah dai ta tabbatar da cewa Aurenta na biyu ya mutu ne a hirar da BBC inda tace mijin nata yaudararta yayi.
Fada Saboda Budurwa yasa an yi asarar rai a Kano

Fada Saboda Budurwa yasa an yi asarar rai a Kano

Duk Labarai
Rahotanni daga Kano sun ce fada da ya barke tsakanin matasan kauyukan Faruruwa dana Tarandai dake karamar hukumar Takai ta jihar yasa an yi asarar rai. Lamarin ya farune a kasuwar garin Faruruwa ranar 23 ga watan Mayu da misalin karfe 7:45 p.m. An yi fadanne ranar Kasuwar garin inda aka kona runfunan Kasuwa da dama. Rahoton yace wani me suna Sani Yunusa, 28 daga kauyen Toho Diribo dake karamar hukumar Takai ya je wajan budurwarsa dake kauyen Tarandai. Saidai matasa sun afka masa da duka da itace. Tuni aka aika da jami'an tsaro yankin dan su kwantar da tarzomar. Rahoton yace ana kokarin kama wadanda suka fara tada tarzomar dan yi musu hukunci.