Thursday, February 13
Shadow

Author: Auwal Abubakar

Mawakin Najeriya, 2face Idibia ya saki matarsa da suka dade tare ya koma soyayya da ‘yar majalisar jihar Edo, Natasha

Mawakin Najeriya, 2face Idibia ya saki matarsa da suka dade tare ya koma soyayya da ‘yar majalisar jihar Edo, Natasha

Duk Labarai
Tauraron mawakin Najeriya, 2face Idibia ya rabu da matarsa, Annie wadda suka dade tare hadda yara inda a yanzu ya fara soyayya da 'yar majalisar jihar Edo, Natasha Osawaru. 2face ya fito ya bayyanawa Duniya cewa yanzu wadda yake so kuma yake da burin aure itace Natasha Osawaru kuma kada mutane su zargeta da cewa itace silar rabuwarsa da matarsa. https://www.tiktok.com/@beautyqueen_5l/video/7470714448022441238?_t=ZM-8tsO4RaZaFC&_r=1 Bisa Al'adar mutanen kudu, 2face ya nemi Natasha ta aureshi kuma tuni ta amince masa da hakan. Tuni 2face ya baiwa Natasha Zoben Alkawari Lamarin da ya jawo cece-kuce sosaia kafafen sada zumunta.
Wallahi sai da ka dirkawa matarka cikin shege kamin ka aureta kuma idan kace karya nake ka kaini kotu ina da hujja>>Wata Budurwa ta gayawa dan Tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai

Wallahi sai da ka dirkawa matarka cikin shege kamin ka aureta kuma idan kace karya nake ka kaini kotu ina da hujja>>Wata Budurwa ta gayawa dan Tsohon Gwamnan Kaduna, Bashir El-Rufai

Duk Labarai
Takaddama ta barke tsakanin wata budurwa da dan gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Bashir El-Rufai a dandalin X wanda a baya ake kira da Twitter. Budurwar dai me amfani da sunan Felexible Queen ta mayarwa da Bashir Martanine akan maganar da yayi ta shagube kan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu inda tace tasan Shugaba Tinubu ya baiwa 'ya'yansa tarbiyya ba zasu fito suna cin zarafin mutane ba. Ta jawo hankalin Tsohon gwamnan da cewa ya yiwa dan nasa magana kan abinda yake aikatawa. Saidai lamarin ya kazance bayan da bashir ya mayar mata da martanin cewa, tana yawo otal-otal tana biyawa tsaffin mutane da suka kai sa'annin babanta bukata. Ta mayar mai da martanin cewa shi Jahili ne marar addini i da tace kawai zai yi mata kazafine amma bashi da hujja inda ta kara da cewa, "You ...
Kalli Yanda daliba ta mari malaminta saboda ya mata magana akan Bidiyon Tiktok

Kalli Yanda daliba ta mari malaminta saboda ya mata magana akan Bidiyon Tiktok

Duk Labarai
Wata daliba a jami'ar Nnamdi Azikiwe University dake Awka jihar Anambra ta mari malaminta sannan ta cijeshi. Dalibar dai tana daukar bidiyon Tiktok ne sai malamin ya zo wucewa ya mata magana tare da dan tureta. Saidai ta juya ta rika zaginsa da gaya masa kalamai marasa dadi inda shi kuma ya nemi ta goge bidiyon da ta dauka. Saidai ta ki inda ta cukumeshi ta mareshi ta kuma cijeshi, a karshe dai da kyar aka kwaceshi a hannunta inda sai da aka kaishi asibiti. Tuni dai makarantar ta sanar da cewa ta dauki matakin yin bincike akan lamarin kamin tasan hukuncin da zata yanke. Kalli Bidiyon faruwar lamarin anan
Na yi nadamar yiwa Tinubu yakin neman zabe, Jama’a ku yafe min kan jawo hankalinku da na yi kuka zabeshi>>Dan Balki Kwamanda

Na yi nadamar yiwa Tinubu yakin neman zabe, Jama’a ku yafe min kan jawo hankalinku da na yi kuka zabeshi>>Dan Balki Kwamanda

Duk Labarai
Dan siyasa a jiar Kano, Dan Balki Kwamanda ya bayyana nadama kan jawo hankalin mutane da yayi suka zabi shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin shugaban kasa. Yace yayi nadamar yakin neman zaben da yawa Tinubu. Yace tunda yake a rayuwarsa bai taba yin abinda yayi nadamarsa sosai ba kamar yiwa Tinubu yakin neman zabe. Yace dalili kuwa shine alkawuran da Bola Ahmad Tinubu ya dauka be cika ba kuma mutane na cikin matsananciyar wahala. Ya bayyana hakane a watan hira da gidan Jaridar Daily Trust suka yi dashi inda yace yana neman yafiyar wadanda ya yaudara.
Bìndìgù Sama da Dubu uku sun bace a hannun ‘yansandan Najeriya

Bìndìgù Sama da Dubu uku sun bace a hannun ‘yansandan Najeriya

Duk Labarai
Majalisar tarayya ta tuhumi shugaban 'yansandan Najeriya, (IGP),  Kayode Egbetokun bisa bacewar Bindigu 3,907 a hannun 'yansandan. Hakanan an masa tambayoyi game da aikata ba daidai ba da kudi a shekarar 2019. Shugaban 'yansandan da farko ya baiwa majalisar hakuri kan rashin amsa gayyatar da suka masa. Sannan ya wakilta mataimakinsa, AIG Suleiman Abdul ya wa 'yan majalisar jawabi kan tambayoyin batan kudaden da suke masa. Saida ya kasa bayar da gamsashshiyar amsa game da bacewar Bindigun inda suka nemi a shiga tattaunawar sirri a kori 'yan jarida daga dakin taron. Saidai 'yan majalisar sun ki amincewa da wannan kira inda suka ce shugaban 'yansandan ya kkma ya nemo amsar tambayoyin da suka masa.
Kalli Hotuna: Ana zargin Gwamnan Najeriya da dirkawa wata ‘yar Fim ciki

Kalli Hotuna: Ana zargin Gwamnan Najeriya da dirkawa wata ‘yar Fim ciki

Duk Labarai
Juna-biyun da na ke ɗauke da shi ba shi da alaƙa da wani gwamna - Jaruma Nengi Nengi Hampson, tsohuwar jaruma a shirin fim na gasar Big Brother Naija (BBNaija), ta karyata jita-jitar da ke yawo a kafafen sadarwa cewa tana dauke da juna biyu da wani gwamna a Najeriya ya yi mata. Jaridar TheCable ta rawaito cewa rahotannin farko sun yi ikirarin cewa jarumar mai shekara 27 ta haifi jariri ga wani gwamna mai shekara 65 kuma har ta zama matarsa ta biyar. A wani rubutu da ta wallafa kwanan nan a shafin X, Nengi ta bayyana takaicinta game da wannan jita-jita, tana mai cewa da ta sani ma da ta kau da kai daga jita-jitar. Sai dai ta ce dole ta yi magana saboda abin ya shafi mutanen da ta ke girmamawa sosai. Jarumar ta jaddada cewa ba za ta bari wannan jita-jita ta bata rayuwarta ko t...
Matsin Tattalin Arziki yayi yawa, ‘Yan Najeriya ba zasu iya biya ba>>Majalisar Tarayya tacewa Ministan sadarwa maza a dakatar da karin kudin kiran waya da ake shirin yi

Matsin Tattalin Arziki yayi yawa, ‘Yan Najeriya ba zasu iya biya ba>>Majalisar Tarayya tacewa Ministan sadarwa maza a dakatar da karin kudin kiran waya da ake shirin yi

Duk Labarai
Biyo bayan karin kudin kiran waya dana data da kamfanonin sadarwa suka yi, majalisar tarayya ta yunkuro dan dakatar da karin. Hukumar sadarwa ta kasa, NCC tuni ta amincewa kamfanonin sadarwar su kara kaso 50 cikin 100 na kudin da suke caji. Saidai kungiyoyin fafutuka da suka hada dana Kwadago, NLC da TUC sun ce basu amince da wannan kari ba. 'Yan majalisar ta wakilai a ranar Talata sun baiwa ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani umarnin ya dakatar da kari kudin kiran wayar inda suka ce 'yan Najeriya ba zasu iya biya ba musamman a wannan yanayi na matsin tattalin arziki. Sai ranar Litinin me zuwa ne ya kamata a fara yin karin kudin kiran dana data, amma MTN a matsayin kamfanin sadarwa mafi girma a Najeriya Tun a wannan satin sun fara kara kudin kira. A wata hira da ja...