Friday, December 5
Shadow

Ba a ga watan Zulki’ida ba a Najeriya – Fadar sarkin Musulmi

Fadar Sarkin Musulmi a Najeriya Muhammad Sa’ad Abubakar III ta ce ranar Talata ce 1 ga watan Zulki’ida na shekarar Hijira ta 1446.

Wata sanarwa da shugaban kwamatin ganin wata na fadar, Farfesa Sambo Wali ya fitar ta ce an ɗauki matakin ne saboda ba a ga jaririn watan ba a ranar Lahadi.

A ƙa’idar kalandar Musulunci, kowane wata yana yin kwana 29 ne, amma idan ba a ga jaririn watan ba sai a cika shi zuwa kwana 30.

Hakan na nufin yau Litinin 28 ga watan Afrilu ne 30 ga watan Ƙaramar Sallah na Shawwal.

Karanta Wannan  Kungiyoyin kare hakkin masu amfani da wayoyin hannu sun maka Gwamnati a kotu saboda karin kudin kiran waya da kaso 50

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *