Thursday, May 22
Shadow

Ba ‘yan Bindiga bane mune: Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi karin haske kan Jirgin samansu da aka gani a daji

Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi karin haske kan Bidiyon da ya yadu sosai a kafafen sada zumunta inda aka ga jirgin samansu yana sauka da tashi a tsakanin wasu masu rike da makamai.

An yi zargin cewa jirgin ya je kaiwa ‘yan Bindiga kayan abinci da sauran kayan aiki ne.

Saidai a sanarwar da ta fitar ta shafinta na sada zumunta, Hukumar ‘yansandan tace ba ‘yan Bindiga bane aka gani a cikin Bidiyon ba. ‘Yansanda ne dake aikin samar da tsaro a dajin Obajana na jihar Kogi.

Hukumar tace a daina dogaro da bayanan da basu fito daga bakin hukumomin tsaro ba dan gujema labarin karya.

Karanta Wannan  Amaryar Rarara Kenan, Malama Sayyada Aisha Humaira A Wajen Liyafar Da Ta Shirya Na Yabon Annabi Muhammad (S.A.W) A Jihar Borno A Jiya Alhamis

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *