Monday, April 6
Shadow

Ba zamu yadda kasar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba>>Inji Kasashen G7

Rahotanni daga kasar Canada inda aka yi taron kasashe 7 mafiya karfin tattalin Arziki wadanda ake kira da G7 sun bayyana cewa, ba zasu amince kasar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba.

Kasashen sun ce suna son a samu zaman lafiya a gabas ta tsakiya kuma sun amince kasar Israyla na da damar kare kanta.

Sun bayyana cewa kasar Iran itace ummul aba isin rashin zaman lafiyar da ake fama dashi a yankin na gabas ta tsakiya.

Dan haka suna jaddada matsayarsu ta cewa ba zasu amince kasar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba.

Kasashen G7 da shuwagabannin su sune kamar haka:

Karanta Wannan  Muna nan akan Bakanmu, kowa sai ya biya Haraji, ko ta hanyar halarar ya samu kuri ko bata ta hanyar halal ba, Qaruwai, Kwandastan Mota, dama kowace irin sana'a kake nan da 2026 sai ka fara biyan Haraji>>Inji Gwamnatin Tinubu

Donald J Trump (The USA)
Keir Starmer (The UK)
Friedrich Merz (German Chancellor)
Giorgia Meloni (Italy PM)
Emmanuel Macron (France)
Shigeru Ishiba (Japan PM)

Wasu kasashen Duniya da aka gayyata zuwa wannan taro sun hada da Australia, South Korea, Brazil, India, Mexico, Ukraine da South Africa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *