Friday, December 5
Shadow

Babu kotun da ke da hurumin tursasa mutane su yi aure dole>>Inji Kungiyar Lauyoyi ta kasa, NBA akan maganar auren Maiwushirya da ‘YarGuda

Rahotanni sun bayyana cewa, Kungiyar lauyoyin Najeriya, NBA ta fitar da matsaya game da auren ‘YarGuda da Maiwushirya.

Kungiyar tace ta samu labarin auren wanda wata kotun Magistrate ta yi a Kano.

Tace babu wata kotu dake da hurumin tursasa mutum yayi aure saboda hakan take hakkin bil’adama ne saboda aure abune wanda mutum ke yi saboda akwai soyayya da fahimtar juna tsakanin masoyan.

Dan haka NBA tace tana neman a sake duba wannan hukunci dan tabbatar ba’a takewa wanda lamarin ya shafa ba hakkinsu.

Saidai Rahotanni sun nuna cewa, Maiwushirya da kanshi ne yace zai auri ‘YarGuda inda itama ta amince da hakan.

Karanta Wannan  Kwanannan Gwamnatin Tinubu zata koma neman bashi a wajan Opay>>Inji Sanata Dino Melaye

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *