
Hukumar shirya jarabawar Jami’a ta JAMB sun bayyana cewa, ba gaskiya bane rahotannin dake yawo cewa wai sun daga jarabawar ta JAMB.
Hukumar tace ranar da aka saka ta rubuta jarabawar na nan ba canji.
JAMB ta saka ranekun Alhamis 16 ga watan Afrilu zuwa Asabar 25 ga watan dan rubuta jarabawar.