Tuesday, February 24
Shadow

Duk Labarai

Yawancin Talakawan Najeriya basa samun Tallafin da Gwamnatin tarayya tace tana bayarwa>>Inji Bankin Duniya

Yawancin Talakawan Najeriya basa samun Tallafin da Gwamnatin tarayya tace tana bayarwa>>Inji Bankin Duniya

Duk Labarai
Bankin Duniya ya fitar da rahoto kan yanda ake raba tallafin rage radadin Talauci ga talakawa. Bankin yace kaso 44 cikin 100 ne kacal na mutanen da aka ce ana baiwa tallafin ke samun sa. Bankin yace kuma ko abincin da ake ciyar da dalibai ya kamata a karashi. Hakan na zuwane bayan da ministan kudi Wale Edun yace sun raba naira 25,000 ga mutane Miliyan 8.5 inda ya kara da cewa akwai sauran mutane Miliyan 6.5 da zasu biya nan da karshen shekara. Bankin Ya nuna damuwa kan yanda Najeriya ke kasancewa tana dogaro da kasashen waje wajan samun kudin da zata tallafawa Talakawanta.
Sojan Najeriya da ya hana Ministan Abuja, Nyesom Wike shiga waja dake gini dan ya rusashi nata shan yabo wajan ‘yan Najeriya

Sojan Najeriya da ya hana Ministan Abuja, Nyesom Wike shiga waja dake gini dan ya rusashi nata shan yabo wajan ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Sojan Ruwan Najeriya, Lieutenant A.M. Yerima na shan yabo bayan Tirka-Tirkar da suka yi da ministan Abuja, Nyesom Wike kan sai ya shiga wajan wani gini ya hana amma sojan ya hanashi shiga. Wike ya kira har shugaban tsaro gaba daya na kasa amma Sojan yawa Shugaban bayanin cewa na sama dashi ne ya sashi wannan aiki. Saidai Wike ya koma yana zagin sojan da cewa, wawa ne amma sojan yace shi ba wawa bane. Wani daga cikin yaran Wike ya gayawa sojan cewa ba zaka yi shiru ba oga na magana kana magana, Shina Wike din yace masa yayi Shiru amma yace ba zai yi shiru ba. Lamarin ya dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda da dama suka yabawa sojan. Saidai wasu daga cikin yaran Wike sunce sojan ya sabawa ka'idar aiki inda suke cewa hakan daidai yake da yunkurin yin juyin mulki. ...
Kalli Bidiyon: Tauraron fina-finan Hausa, KB International ya fito yayi bayani bayan Bidiyonsa ya bayyana yana cewa, zai iya yin Tallar Ghiya akan Naira Miliyan 50

Kalli Bidiyon: Tauraron fina-finan Hausa, KB International ya fito yayi bayani bayan Bidiyonsa ya bayyana yana cewa, zai iya yin Tallar Ghiya akan Naira Miliyan 50

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, KB International ya fito yayi magana bayan da Bidiyonsa ya bayyana aka ga yana cewa zai iya yin tallar Giya akan Naira Miliyan 50. KB a Bidiyon jawabinsa yace datse Bidiyon aka yi inda yace suna maganane kuma wasa ake. Ga cikakken bayaninsa kamar haka: https://www.tiktok.com/@kb_international/video/7571074899826035976?_t=ZS-91JcALCMqkj&_r=1
Wasan cin kofin Kwallon kafa na Duniya na 2026 shine na karshe da zan buga>>Inji Cristiano Ronaldo

Wasan cin kofin Kwallon kafa na Duniya na 2026 shine na karshe da zan buga>>Inji Cristiano Ronaldo

Duk Labarai
Tauraron da kwallon kasar Portugal, Cristiano Ronaldo ya bayyana cewa, wasan cin kofin kwallon kafa na Duniya na shekarar 2026 shine na karshe da zai buga. Ronaldo ya bayyana hakane a waa hira da aka yi dashi daga kasar Saudiyya a wajan wani taro na yawon bude ido da zuba hannun Jari. Hakanan Ronaldo ya sanar da cewa, nan da shekaru 2 zai daina buga kwallonnkafa.
Kalli Bidiyon, Yanda hankula suka tashi bayan sojoji sun hana Wike Shiga wani Fili a Abuja

Kalli Bidiyon, Yanda hankula suka tashi bayan sojoji sun hana Wike Shiga wani Fili a Abuja

Duk Labarai
Hankula sun tashi akaita musayar yawu bayan da sojoji suka hana Ministan Abuja, Nyesom Wike shiga wani fili da ake rikici akansa. Sojojin sunce shugabansu, Shugaban Sojojin Ruwa watau Vice Admiral Zubairu Gambo ne ya basu umarni. Saidai Shugaban tsaro na kasa ya shiga lamarin aka sasanta kamin abun ya kazance. https://twitter.com/emmaikumeh/status/1988232078660350319?t=aMVL1A0a5ASt688z4sH_Jg&s=19
Kalli Sabon Bidiyon Dan majalisa Alhassan Ado Doguwa a Landan yana Kwambo daya dauki hankula inda a wannan karin aka ganshi yana cin abinci a bandaki

Kalli Sabon Bidiyon Dan majalisa Alhassan Ado Doguwa a Landan yana Kwambo daya dauki hankula inda a wannan karin aka ganshi yana cin abinci a bandaki

Duk Labarai
A dasu da safene aka ga Bidiyon Alhassan Ado Doguwa yana kwambo a kan titin Birnin Landan na kasar Ingila. Lamarin ya jawo cece-kuce inda mutane sukai ta mamakin dan majalisar Tarayya guda da nuna irin wannan halayya. Saidai ashe kallo be kare ba, a karo na biyu an ga Doguwa yana daukar hoton a cikin dakin Otal dib da ya sauka inda a wannan karin har abinci yaci a cikin bandaki. https://twitter.com/Asad_Mukty/status/1988160598086164882?t=k_sh_5vZZm33_Yz-mo4w3Q&s=19
Mutuncin Najeriya ya zube a Idon Duniya, A lokacin ina shugaban kasa, Amurka basa yin komai a Afrika ba tare da sun sanar da Najeriya ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Obasanjo

Mutuncin Najeriya ya zube a Idon Duniya, A lokacin ina shugaban kasa, Amurka basa yin komai a Afrika ba tare da sun sanar da Najeriya ba>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Obasanjo

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana damuwa kan yanda Darajar Najeriya ta zube a Idon Duniya inda yace a lokacin mulkin sa da Marigayi Janar Murtala, Kasar Amurka basa daukar wani mataki a Afrika ba tare da Sanar da Najeriya ba. Ya bayyana hakane a Abeokuta ranar Litinin yayin ganawa da wasu matasa. Obasanjo yace shi da Murtala sun dawo da Martabar Najeriya . Yace a lokacin da aka baiwa Najeriya 'yancin kai Turawa na ganin itace giwar Africa kuma suna girmama ta amma daga baya wannan girman ya dusashe. Obasanjo yayi kira ga matasa da su tashi tsaye su karbe mulki daga hannun tsaffin dake mulkar Najeriya a yanzu yace amma idan suka bari abubuwa suka ci gaba da faruwa a haka, babu inda kasar zata.
A rika yin aure yanda Addini ya tanada: Tsarabe-Tsaraben da ake kawowa ne yasa aure be dadewa yake mutuwa>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma’u Wakili

A rika yin aure yanda Addini ya tanada: Tsarabe-Tsaraben da ake kawowa ne yasa aure be dadewa yake mutuwa>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma’u Wakili

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Asma'u Wakili ta bayar da shawarar a rika yin aure kamar yanda addinin Musulunci ya tanada inda tace tsarabe-tsaraben da ake yi na wasu shagulgulan da suka sabawa Addini wani bin su ne ke kawo mutuwar aure da wuri. Ta bayar da shawarar ne a shafinta na sada zumunta inda tace tasan zata sha martani. https://www.tiktok.com/@asmee_wakili/video/7571186756314320136?_t=ZS-91J25LB8g9g&_r=1
Har yanzu ina nan inata kokarin ganawa da Trump tun bayan Bharazanar da yawa Najeriya>>Shugaba Tinubu

Har yanzu ina nan inata kokarin ganawa da Trump tun bayan Bharazanar da yawa Najeriya>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa har yanzu yana kokarin ganawa da shugaban kasar Amirka, Donald Trump. Ya bayyana hakane ta bakin me bashi shawara kan harkar sadarwa, Watau Daniel Bwala a hirar da aka yi dashi a Arise TV. Daniel Bwala yace kwanannan Shugaba Tinubu da Donald Trump zasu gana dan karfafa dangantakar Najeriya da kasar ta Amurka. Ya bayyana cewa ba zai bayyana irin shirin da suke ba amma mutane au fahimci cewa har yanzu suna kokarin ganin an bi hanyar data dace dan ganawa tsakanin shuwagabannin biyu.