Dalibai ‘yan mata na jihar Kebbi Duk Musulmai ne, Karanta Jadawalin sunayensu
Hukumomi a jihar Kebbi sun musanta kalaman da wani ɗan majalisar Amurka ya yi cewa akwai yiwuwar ɗaliban da aka sace a jihar mabiya addinin Kirista ne.
Shugaban ƙaramar hukumar Danko/Wasagu, inda lamarin ya faru, Hon Hussaini Bena, ya tabbatar da cewa dukkanin ƴan matan da aka sace, da mai gadin makarantar da aka harbe duk Musulmai ne.
A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X, ɗan majalisar Amurkar Riley Moore ya buƙaci magoya bayansa su taya shi yi wa ƴan matan da aka sace da mutumin da aka kashe addu'a.
A cewarsa '' duk da ba mu da cikakken bayani game da lamarin, amma mun san an kai harin ne a wani yanki da ke da kiristoci da yawa a Arewacin Najeriya, wajibi ne gwamnati ta ƙara ƙoƙari wajen kawo ƙarshen wannan zaluncin''.
A ranar Litinin da asuba ne wasu ƴanbindiga riƙe d...








