Saturday, May 10
Shadow

Cikin sauki zan sake cin zabe a shekarar 2027, ‘Yan Najeriya sun shaida kokarina, kar har Kungiyoyin Duniya irin su IMF sun jinjina min>>Shugaba Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya mayarwa da dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar Labour party, Datti Baba Ahmad martani bayan da yace idan shugaban kasar na da wayau kada ya tsaya takarar shugaban kasa a 2027 saboda faduwa zabe zai yi.

A martaninsa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yace maganar Datti ta banza ce wadda ba basira ko kadan a ciki.

Da yake magana da bakin kakakinsa, Daniel Bwala, Shugaba Tinubu yace Datti Ahmad ya daina shiga harkar da bai iya ba, watau siyasa, ya barwa wanda suka iya su yi.

Yace yayi kokari sosai na daukar matakan gyara wanda ‘yan Najeriya sun shaida kuma har kungiyoyin Duniya irin su IMF sun jinjina masa inda suka ce ya Dora Najeriya a turbar karfafa tattalin arziki.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Cikin sheshshekar kuka wannan matar tana rokon Dan Allah wani ya fito ya aureta, tace Wallahi ta tuba ba zata kara yin rawar badala a intanet ba, tace kuma zata baiwa duk wanda ya yadda ya aureta naira Miliyan 20

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *