Wednesday, April 8
Shadow

Da Duminsa: Gwamnonin Arewa zasu Gana a Kaduna game da matsalar tsaron da ta addabi yankin

Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnonin Arewacin Najeriya zasu gana a Kaduna saboda tattaunawa matsalar tsaro da ta addabi yankin.

Rahoton yace hadimin gwamnan jihar Gombe, Ismaila Misilli ne ya bayyanawa manema labarai na Punchng hakan inda yace gwamnan Gomben shine ya kira wannan taron a matsayinsa na shugaban Gwamnonin Arewan.

Yace idan dai ba an canja ba, a yau, Asabar ne za’a yi wannan taro a Kaduna kuma matsalar tsaron yankin ce babban abinda za’a tattauna.

Karanta Wannan  Mun godewa Allah da kafuwar Jam'iyyar ADC, saboda ta fito mana da bakaken munafukan cikin jam'iyyar mu ta APC wanda suka Munafurci Tinubu a zaben 2023 Karara mun gansu>>Inji Ministan Sufurin Jiragen sama, Festus Keyamo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *