Sunday, December 14
Shadow

Da Duminsa: Jami’an tsaro sun kama Rikakken Dan Bìndìgà da ake nema ruwa a jallo cikin maniyyata yana shirin zuwa aikin Hanjji

Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja sun bayyana cewa, jami’an tsaro sun kama rikakken dan Bindiga da ake nema ruwa a Jallo cikin maniyyatan da ake tantance wa.

Sunan wanda aka kama din shine Yahaya Zango wanda jami’an tsaro sun jima da saka sunansa cikin wadanda ake nema ruwa a jallo.

Ya je wajan tantance Alhazai inda ya bayar da fasfo dinsa nan kuwa jami’an DSS suka yi ram dashi aka wuce ofis dashi, kamar yanda Jaridar daily Trust ta ruwaito.

Karanta Wannan  Jam'iyyar PDP ta lashe gaba dayan zaben kananan hukumomin da aka gudanar a jihar Osun

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *