Monday, April 27
Shadow

Da Duminsa: Jami’an tsaro sun kama Rikakken Dan Bìndìgà da ake nema ruwa a jallo cikin maniyyata yana shirin zuwa aikin Hanjji

Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja sun bayyana cewa, jami’an tsaro sun kama rikakken dan Bindiga da ake nema ruwa a Jallo cikin maniyyatan da ake tantance wa.

Sunan wanda aka kama din shine Yahaya Zango wanda jami’an tsaro sun jima da saka sunansa cikin wadanda ake nema ruwa a jallo.

Ya je wajan tantance Alhazai inda ya bayar da fasfo dinsa nan kuwa jami’an DSS suka yi ram dashi aka wuce ofis dashi, kamar yanda Jaridar daily Trust ta ruwaito.

Karanta Wannan  A dakin Otal Muka kama Nnamdi Kanu yana hutawa da wata mata>>Gwamnatin Tarayya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *