Monday, March 17
Shadow

Da Duminsa: ‘Yan Bìndìgà sun sako janar Maharazu Tsiga

Rahotanni sun bayyana cewa, ‘yan Bindiga da suka yi garkuwa da tsohon shugaban hukumar bautar kasa, Janar Maharazu Tsiga sun sakoshi.

An sakoshi ne bayan shafe kwanaki 22 a hannun masu garkuwa da mutanen, Rahoton yace wata majiya tace an sakoshi kuma yana wani asibiti da ba’a bayyana sunansa ba yana jinya.

A ranar 6th February 2025 ne ‘yan Bindigar suka dira a gidansa suka yi garkuwa dashi tare da jikkata mutane 2 sannan daya daga cikin ‘yan Bindigar ya mutu bayan da wani dan Bindigar ya harbeshi bisa kuskure.

A baya dai hutudole ya jiyo cewa ‘yan Bindigar sun nemi kudin fansa Naira Miliyan 250 kamin sakin tsohon sojan.

Karanta Wannan  Banson kasata Ingila ta zama kamar matalauciyar kasa Najeriya>>Inji Kemi Badenoch

Saidai zuwa yanzu hukumomin tsaro a jihar basu ce uffan ba kan lamarin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *