Wednesday, May 7
Shadow

Da Duminsa: Zanga-zanga ta barke a Jos, babban birnin jihar Filato saboda yawaitar Kàshè-Kàshè

Rahotanni daga jihar Filato na cewa, zanga-zanga ta barke a babban birnin jihar watau, Jos saboda yawaitar kashe-kashen ‘yan Asalin Jihar da ake zargin ‘yan Bindiga Fulani da aikatawa.

Babban Limamin kirista, Rev. Polycarp Lubo ne ya jagoranci zanga-zangar wadda aka fara ta daga Titin Fawvwei Junction wanda hakan ya kawo tsaikon ababen hawa.

Daya daga cikin masu zanga-zangar me suna Gyang Dalyop ya shaidawa kafar Punchng cewa, sun fito ne saboda basa jin dadin abinda ke faruwa na kashe-kashen a garuruwansu.

Itama wata me suna Hannatu Philip tace suna kira ga hukumomi su dauki matakan kawo karshen lamarin kamin ya kazance.

Karanta Wannan  A karin farko, Shugaba Tinubu ya sakawa dokar haramtawa sojojin Najariya yin Luwadi, Madigo da shan giya

A wani lamari me alaka da wannan, Hutudole ya kawo muku cewa, a yau ne ake sa ran mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima zai kai ziyara jihar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *