Sunday, April 13
Shadow

DOLE MU YI JINJINA A GARE SU: Sun Biya Dukkan Bashin Da Ake Bin Marigayi Sheik Idris Da Kudin Aljihunsu

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Daga Datti Assalafiy

Lokacin da Allah Madaukakin Sarki ya zare ran babban Malamin Tauhidi na Afirka Sheikh Dr Idris Abdul-Aziz Bauchi, wadannan manyan Malamai wato Sheikh Dr Ibrahim Disina da Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Gurumtum suna samun labari suka taho gidan Malam.

Sannan sukace a tattaro musu list na mutanen da suke bin Malam bashi zasu biya daga aljihunsu, basa bukatar a biya bashin da kudin Malam.

Wallahi wadannan Malamai basu bari an yiwa Malam Sallar jana’iza ba sai da suka biya duk bashin da ake binsa, kana zuwa da shaida da ta tabbatar kana bin Malam bashi nan take suke biya komin yawan kudin.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon wata kalar halitta da wani mutum ya ajiye a gidansa yana tsafi da ita dan neman Duniya

Lokacin da jinyar ajali ta kama Malam zai yafi Kasar Egypt jinya, ya fara neman visa, sai daga baya aka canza shawara a wuce Kasar Indiya kawai, kuma haka akayi, to daga baya visa na Egypt ta fito, suma sun aiko da lissafin kudi a matsayin bashi da suke bin Malam, kuma wadannan Malamai sun biya.

Kowa ya sani Malam yana da dunbin dukiyar da za’a biya masa bashin da ake binsa, amma wadannan Malamai sukace kar a biya da kudin Malam su zasu biya da kudinsu, idan ba cikakken masoyinka na gaskiya ba babu wanda zai maka haka.

A rayuwa baka fahimtar waye cikakken masoyinka sai ranar da ka fada cikin jarrabawa ta rayuwa, ko kuma sai bayan ka mutu a lokacin ne masoyanka na gaskiya zasu biya maka bashin da ake binka, sannan su kula da iyalanka.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo:Soja ya bace bayan da ya zargi cewa sojojin da aka jiwa rauni a wajan aiki da kudaden Aljihunsu suke kula da kansu a Asibitoci

Muna rokon Allah Ya saka musu da Aljannah.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *