Thursday, February 5
Shadow

Fadar Shugaban kasa ta nuna bacin rai sosai sannan ta nemi Kwankwaso ya baiwa Shugaba Tinubu Hakuri kan ikirarin da yayi cewa Tinubu na nunawa Arewa wariya a mulkinsa

Fadar Shugaban kasa ta bukaci Kwankwaso ya bayar da hakuri ga Tinubu, ya janye maganganunsa kan Gwamnati

Daga Ayau News

Ministan Ayyuka, Injiniya David Umahi, ya bukaci tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, da ya bada hakuri ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan kalaman da ya yi game da gwamnati.

Ayau News ta ruwaito Umahi ya ce maganganun Kwankwaso na zargin gwamnati tana fifita kudu ba su dace ba. Ya bukace shi da ya janye su domin gujewa rarrabuwar kawuna a kasa.

Kwankwaso ya zargi gwamnatin Tinubu da nuna fifiko kan yankin kudu, yana cewa an bar Arewa a baya wajen ayyukan cigaba.

Karanta Wannan  Watarana Talakawa Za Su Yi Kukan Rashin Shugaban ƙasa Bola Tinubu A Najeriya, inji fadar shugaban ƙasa

— A Yau News

Me zaku ce?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *