Thursday, December 25
Shadow

Gamayyar su Atiku da El-Rufai watsewa zata yi, ba zasu iya yin nasara akan Tinubu ba>>Inji Tanko Yakasai

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Dattijon jihar Kano, Dr. Tanko Yakasai ya bayyana cewa, gamayyar su Atiku Abubakar, Peter Obi, da Nasir Ahmad El-Rufai ba zasu yi nasara ba akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Ya bayyana hakane a hirar da yayi da ‘yan Jarida a Abuja.

Yakasai wanda shine shugaban kungiyar magoya bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yace babu wanda zai yadda da su Atiku.

Yace saboda a shekarun baya an basu dama su gyara Najeriya amma suka kasa.

Yace a lokacinsu ne aka kashe dala Biliyan $16 dan gyaran wutar lantarkin Najeriya amma bata gyaru ba, sannan yace a lokacinsu ne aka yi badakalar Halliburton har aka daure dan majalisa daga kasar Amurka, amma a Najeriya ba’a daure wadanda suka aikata laifin dashi ba.

Karanta Wannan  Wani ɗan asalin jihar kano, mazaunin Faransa ya kafa sabon tarihi a fannin kimiyya

Yace maimakon su Atiku su zo su hada kai da Tinubu da yazo gyaran wadancan kura-kurai da suka tafka, amma sai auke hadaka dan kara kwace mulki daga hannunsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *