Friday, December 5
Shadow

Gamayyar su Atiku da El-Rufai watsewa zata yi, ba zasu iya yin nasara akan Tinubu ba>>Inji Tanko Yakasai

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Dattijon jihar Kano, Dr. Tanko Yakasai ya bayyana cewa, gamayyar su Atiku Abubakar, Peter Obi, da Nasir Ahmad El-Rufai ba zasu yi nasara ba akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Ya bayyana hakane a hirar da yayi da ‘yan Jarida a Abuja.

Yakasai wanda shine shugaban kungiyar magoya bayan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yace babu wanda zai yadda da su Atiku.

Yace saboda a shekarun baya an basu dama su gyara Najeriya amma suka kasa.

Yace a lokacinsu ne aka kashe dala Biliyan $16 dan gyaran wutar lantarkin Najeriya amma bata gyaru ba, sannan yace a lokacinsu ne aka yi badakalar Halliburton har aka daure dan majalisa daga kasar Amurka, amma a Najeriya ba’a daure wadanda suka aikata laifin dashi ba.

Karanta Wannan  Da Dumisa: Kasar Sifaniya ta bi sahun kasar Afrika ta kudu wajan kai karar kasar Israyla kan kìsàn kiyashin da takewa Falasdiynawa

Yace maimakon su Atiku su zo su hada kai da Tinubu da yazo gyaran wadancan kura-kurai da suka tafka, amma sai auke hadaka dan kara kwace mulki daga hannunsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *