Thursday, January 15
Shadow

Gwamnatin Tarayya ta hada kai da matatar man fetur din Dangote dan rage farashin man

Shugaba kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bukaci a rage farashin man fetur a Najeriya.

Kuma hukumar kula da sayar da man fetur din Najeriya, NEPZA a takaice ta bayyana aniyarta ta hada kai da matatar man fetur din Dangote dan tabbatar da wannan bukata ta shugaban kasa.

Shugaban hukumar, Dr. Olufemi Ogunyemi ne ya bayyana haka a Abuja yayin wata ziyara da aka kai masa.

Itama matatar man Dangote ta ce a shirye take dan tabbatar da wannan kudirin na shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

Wannan shiri zai samu nasara ne ta hanyar tabbatar da ci gaba da sayar da man fetur din Najeriya da kudin Naira maimakon dala musamman ga matatar Dangote.

Karanta Wannan  DA DUMIDUMINSA: Gwamna Bala Na jihar Bauchi Ya Bada Umurnin A Mayarwa Da Almajiran Marigayi Sheikh Idris Dutsen Tanshi Filin Idi Na Games Village Da Aka Kwace A Baya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *