Friday, January 2
Shadow

Gwamnoni na farin ciki da cire tallafin man fetur kuma in ku baku jin dadi, su suna jin dadin cire tallafin>>Inji Me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala

Me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala ya bayyana cewa, Gwamnonin Najeriya na jin dadin cire tallafin man fetur da aka yi.

Yace a yanzu babu Gwamnan da baya iya biyan ma’aikatan jiharsa Albashi.

Yace maimakon a baya wanda gwamnoni kusan sama da 20 ne basa iya biyan Albashi.

Daniel Bwala ya bayyana hakane a yayin zantawar da aka yi dashi a gidan Talabijin na chan TV.

Ya kuma ce gwamnonin a yanzu suna samun kudaden gudanar da ayyuka a jihohinsu ba kamar a baya ba.

Karanta Wannan  Manyan Sojojin Amurka sun gargadi shugaban kasar, Donald Trump da cewa akwai yiyuwar ko sun kawo Khari Najeriya ba zasu yi nasara ba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *