Saturday, December 13
Shadow

Hotunan mata 2 da suka fito takarar shugaban kasa a kasar Iran

Mata biyu ne suka fito takarar shugaban kasa a kasar Iran biyo bayan rasuwar tsohon shugaban kasar, Ebrahim Raisi a hadarin jirgin sama me saukar Angulu.

Mace ta farko itace Zohre Elahian wadda ‘yar majalisar tarayyar kasar ce kuma tana da karatu har zuwa digiri na 3 watau(Doctorate) a fannin physics.

Sai kuma mace ta biyu me suna, Hamideh Zarabadi wadda itama ‘yar majalisar tarayyar kasar ce kuma tana da digiri na 3 watau( Doctorate) a fannin engineering.

Saidai kasancewar Iran kasar Musulmi ce da take riko da addinin musulunci sosai da kamar wuya su yadda su zabi mace a matsayin shugaban kasa.

Karanta Wannan  Kungiyar 'yan kasuwar man fetur, IPMAN ta yi baranzanar tsayar da aiki saboda karin kudin man feturninda tace hakan ya kara jefa 'yan Najeriya wahala

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *