Saturday, May 17
Shadow

Hukumar kula da sararin samaniya ta Najeriya ta yi hasashen samun Gajimare da tsawa a fadin kasar

Hukumar sararin samaniya ta Najeriya, (NiMet) ta yi hasashen samun Gajimare da rana a wasu sassan Najeriya daga ranar Laraba har zuwa Juma’a.

A sanarwar data fitar ranar Talata a Abuja, Hukumar tace za’a samu rana a jihohin Arewa daga ranar Laraba zuwa Juma’a.

Tace amma za’a iya samun hadari a sararin samaniyar jihohin Kaduna, Adamawa, Sokoto, Kebbi, Zamfara da Taraba da kuma tsawa.

Hakanan tace a jihohin Benue, Plateau, Niger, Kwara da Kogi ma abinda ake tsammanin zai faru kenan.

A jihohin Delta, Cross River, Akwa Ibom, Rivers da Bayelsa kuma sun ce za’a samu hasken rana da safe inda suma ana tsammanin Hadari da tsawa.

A jihohin Kebbi, Taraba, Borno da Adamawa kuwa hukumar tace za’a tashi ranar Alhamisbda tsawa.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: An kama barawon Akwatin zabe a kasar Amurka

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *