Thursday, February 5
Shadow

Hukumar ‘yansandan farin kaya DSS ta bukaci kafar X ta goge shafin Sowore saboda zarginsa da batawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suna

Hukumar ‘yansandan farin kaya, DSS ta bukaci kafar sada zumunta ta X wadda aka fi sani da Twitter data goge shafin mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore.

Hukumar ta wallafa bukatar hakanne a shafinta na X din inda take zargin Sowore da yada labaran karya da kuma kawo barazanar tsaro saboda wallafa cewa shugaba Tinubu yace ya magance matsalar rashawa da cin hanci a Najeriya amma kuma ba haka bane.

DSS sun ce sun baiwa kafar ta X awanni 24 su goge shafin na Sowore ko kuma su dauki matakin da ya dace akan kafar.

DSS sun ce wannan ikirari na Sowore ya jawo har zanga-zanga an yi wanda hakan yake barazana ga zaman lafiya a Najeriya.

Karanta Wannan  Saudiyya ta ɗauki nauyin kula da alhazan Iran har sai sun samu damar komawa gida

Dan haka sukace Sowore da kafar data bashi dama ya wallafa irin wannan labari na iya fuskantar hukunci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *