Friday, December 5
Shadow

Hukumar ‘yansandan farin kaya DSS ta bukaci kafar X ta goge shafin Sowore saboda zarginsa da batawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suna

Hukumar ‘yansandan farin kaya, DSS ta bukaci kafar sada zumunta ta X wadda aka fi sani da Twitter data goge shafin mawallafin jaridar Sahara Reporters, Omoyele Sowore.

Hukumar ta wallafa bukatar hakanne a shafinta na X din inda take zargin Sowore da yada labaran karya da kuma kawo barazanar tsaro saboda wallafa cewa shugaba Tinubu yace ya magance matsalar rashawa da cin hanci a Najeriya amma kuma ba haka bane.

DSS sun ce sun baiwa kafar ta X awanni 24 su goge shafin na Sowore ko kuma su dauki matakin da ya dace akan kafar.

DSS sun ce wannan ikirari na Sowore ya jawo har zanga-zanga an yi wanda hakan yake barazana ga zaman lafiya a Najeriya.

Karanta Wannan  An kàshè mutane 20 a sabbin hàrè-hàrèn da aka kai jihar Filato

Dan haka sukace Sowore da kafar data bashi dama ya wallafa irin wannan labari na iya fuskantar hukunci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *