Sunday, March 16
Shadow

Hukumomi a jihar Anambra zasu fara kamen mata masu shigar banza

Wata hukumar tsaro a jihar Anambra ta bayyana aniyarta na fara kamen mata dake shigar banza wanda ke yawo babu rigar nono ko dan kamfai a cikin mutane.

An nadi sautin sanarwar inda aka rika yayatashi a kafafen sadarwa.

Hukumar tsaron ta bayyana cewa, Gwamnan jihar, Chukwuma Soludo ne ya bayar da umarnin yin hakan, saidai gwamnatin jihar bata fitar da sanarwa ba game da lamarin.

Sanarwar tace mata masu saka dan kamfai kadai suma za’a fara kamasu.

Karanta Wannan  DPO din 'yansanda ya yanke jiki ya fadi ya mùtù

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *